Duk da Danuwansa Yana Takarar Gwamna, Garo Ya Ce Ba Zai Zabi Jamiyyar APC ba

Publish date: 2024-06-07

Kano - Bello Sule Garo ya bayyana cewa a zabe mai zuwa da a za a shirya, kuri’arsa ta na wajen jam’iyyar hamayya ta NNPP.

Da yake magana a shafinsa na Twitter a Ranar Asabar Bello Sule Garo ya tabbatar da cewa yana tare da jam’iyya mai kayan dadi.

Bello Garo yake cewa ko da babu wanda zai zabi Rabiu Musa Kwankwaso, shi yana goyon bayan ‘dan takaran shugaban kasar.

“Katin PVC na na Kwankwaso ne, ko da kuwa ni kadai ne zan kada masa kuri’a, idan Allah ya so.”

Kara karanta wannan

Rabiu Kwankwaso ya Ziyarci Jihar Arewa Sau 2 a Kwana 15 Domin Samun Kuri’u a NNPP

- Bello Sule Garo

An raba jiha da 'danuwa?

Abin da zai ba wasu mamaki shi ne ‘danuwansa, Murtala Sule Garo yana neman kujerar mataimakin Gwamnan Kano a APC.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Legit.ng Hausa ta fahimci Alhaji Sule Garo, suruki ne ga Rabiu Musa Kwankwaso wanda ya yi gwamna sau biyu a jihar Kano.

Yayin da Murtala Garo yake neman mataimakin Gwamna a karkashin APC, Nasiru Garo da Bello Garo su na tare da Kwanwaso.

Ganin haka ta sa muka tambayi Bello Garo ko zai zabi jam’iyyar NNPP sak, ba zai yi wa ‘danuwansa kara a takarar Gwamna ba.

Wannan Bawan Allah ya tabbatar mana lallai jam’iyya mai kayan dadi za ta samu kuri’unsa a sauran zabukan majalisa da na jiha.

Wannan na mu ne - Kwankwaso Twitter

Abdullahi Ibrahim wanda ya yi suna wajen tallata Rabiu Kwankwaso a dandalin Twitter, ya tofa albarkacin bakinsa a kan batun.

Kara karanta wannan

2023: Kano, Kaduna da wasu jihohi 5 na Arewa duk na Tinubu ne, mataimakin shugaban APC

Malam Abdullahi ya ce ka da sunan ya rudi mutum, Bello Garo yana cikin magoya bayan NNPP da madugun darikar Kwankwasiyya.

Malam Bello Garo yana cikin ‘yan sashen shafukan sada zumunta na kwamitin yakin takarar Abba Kabiru Yusuf a zaben jihar Kano.

Shinkafa da waken Gumsu Abacha

A baya an ji labari 'Diyar tsohon Shuaban Najeriya, Gumsu Abacha ta ce a 2023, Kano sai ‘Dan Soja, a Katsina kuma sai Lado Danmarke.

Gumsu Abacha ta na goyon Muhammad Abacha da Lado Danmarke a PDP domin dayansu 'danuwanta ne, dayan kuma surukinsu.

Asali: Legit.ng

ncG1vNJzZmigkarAonrLnp6irF6jtHC%2FyLKYrJlfZoJyhZdvbWacpaB6pa2MnZinraeWu7StjLKYp5ldqa6srdGaqWafp5a6r62MoJirp12urm6vxGaZmmWqlrZuxsCboGaikaK2usXAq2SaqJNir6J7